in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mahukuntan kasar Sin sun bayyana karfin kasar wajen tabbatar da ganin farashin kaya ya zauna da gindinsa
2011-03-06 17:20:37 cri

Ranar 6 ga wata, Zhang Ping, darektan kwamitin kula da raya kasa da gyare-gyare na kasar Sin, ya furta a nan birnin Beijing cewa, kasar Sin na da karfi wajen tabbatar da ganin farashin kaya ya zauna da gindinsa.

Mista Zhang ya ce, yawancin kayayyakin da ake samarwa daga masana'antun kasar Sin, yawansu ya wuce jimillar da ake bukata a kasuwa.

Ban da haka kuma, Li Yining, dan majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa ta jama'ar kasar Sin, kana shahararren masanin ilimin tattalin arziki na kasar, ya bayyana a ranar 6 ga wata a nan birnin Beijing cewa, matakan da kasar Sin ke dauka a halin yanzu don dakile hauhawar farashin kaya suna da amfani.

A wajen wani taron manema labaru da aka yi a gefen taron shekara-shekara na majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa ta jama'ar kasar Sin, Li Yining ya ce, akwai dalilai da yawa da suka haddasa hauhawar farashin kaya a kasar Sin, wadda ta fara kunno kai a shekarar 2010. Amma yadda kasar ta kara yawan kudin da ya kamata bankuna daban daban su ajiye a babban bankin kasar har sau da dama, ya yi amfani sosai wajen shawo kan hauhawar farashin kaya a kasar.

Mista Li ya kara da cewa, ko da yake ba a samu damar shawo kan sharuda 2 da suke haddasa hauhawar farashin kaya ba, wadanda suka hada da karuwar farashin mai a kasuwannin duniya, gami da dumamar yanayi wadda take addabar aikin gona, amma duk da haka, ta hanyar daukar wasu matakai a gida, za a iya dakile hauhawar farashin kaya, har ma a tabbatar da dorewarsa gwargwadon wani mizani. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China