in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta bayyana ra'ayinta a taron muhalli na MDD
2011-02-22 21:51:19 cri
A ranar 22 ga wata, an ci gaba da gudanar da taron ministoci kan batun kiyaye muhalli a karo na 26 na kwamitin hukumar shirin kiyaye muhalli ta M.D.D a Nairobi,fadar mulkin kasar Kenya, inda tawagar kasar Sin ta bayyana ra'ayinta game da batutuwan raya tattalin arziki tare da kiyaye muhalli, da kyautata muhallin duniya, kana jami'an kasar Sin sun yi mu'amala da bangarorin dake halartar taron kan sauran wasu batutuwan da suka shafi kiyaye muhalli.

Jami'an kasar Sin da suka halarci taron sun ce, kasar Sin a shekarun baya ta gudanar da wasu bincike da gwaje-gwaje don dace da ra'ayin raya kasa tare da kiyaye muhalli, kana ta samu wasu fasahohin, wadanda suka sheda cewa, kafin a yada ra'ayin raya tattalin arziki ba tare da gurbata muhalli ba, dale ne a yi kokarin kafa wani tsarin tattalin arziki mai inganci a duniya, gami da kafa wani tsarin da ake bi wajen gudanar da aikin kyautata muhallin duniya, wanda ya shaida daidaito, sanin ya kamata, da kuma inganci. Kana a yi kokarin sa kaimi ga kasashe masu sukuni da su kara tallafawa kasashe masu tasowa ta fuskar kudi da fasaha.

Taron an kaddamar da shi ne a ranar 21 ga wata, inda ministoci na kasashe sama da 140, da wakilan jama'a gami da manyan jami'ai a harkar kudi suke tattaunawa kan batun bunkasa tattalin arziki ba tare da gurbata muhalli ba da kiyaye muhalli.

Taken taron shi ne bunkasa tattalin arziki ba tare da gurbata muhalli ba, kuma ministocin kula da harkokin kiyaye muhalli na kasashe da dama za su tattauna da yin shawarwari, don rage da kawar da bambancin ra'ayi da ke akwai tsakaninsu wajen kiyaye muhalli. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China