in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kafofin watsa labaru na kasa da kasa sun yaba da ziyarar da shugaba Hu Jintao ya kai kasar Amurka
2011-01-20 20:28:16 cri

Ran 18 ga wata ne, shugaba Hu Jintao na kasar Sin ya sauka Washington, babban birnin kasar Amurka, inda ya fara ziyara aiki a kasar. Kafofin watsa labaru na kasa da kasa sun mai da hankali sosai kan ziyarar Hu Jintao a kasar Amurka, kuma sun yaba ga ziyara tasa.

A wannan rana, yawancin manyan kafofin watsa labaru na kasar Amurka sun bayar da cikkaken rahotanni kan ziyarar Hu Jintao. Gidan telibijin na CNN na kasar Amurka ya ruwaito bayanan babbar sakatariyar harkokin waje ta kasar Amurka Hillary Clinton cewa, tattalin arzikin kasashen Amurka da Sin suna cudar juna, haka ma kuma makomar kasashen biyu.

Kamfanin dillancin labaru na AFP na kasar Faransa ya bayar da rahoto cewa, ziyarar shugaba Hu Jintao ta alamta cewa dangantaka tsakanin kasashen biyu ta kai wani sabon mizani.

Kamfanin dillancin labaru na Reuter ya ce, matsayin tattalin arzikin kasar Sin ya zama na biyu a duniya, ziyarar shugaba Hu Jintao a kasar Amurka a wannan karo ta kasance ziyara mafi muhimmanci a cikin shekaru 30 da suka wuce. [Musa Guo]

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China