in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hu Jintao ya bar birnin Beijing don kai ziyara a kasar Amurka
2011-01-18 15:12:21 cri
Bisa gayyatar da shugaban kasar Amurka Barack Obama ya yi masa, a ran 18 ga wata da yamma, shugaban kasar Sin Hu Jintao ya bar birnin Beijing, don ziyarar aiki a kasar Amurka.

Bisa labarin da ma'aikatar harkokin waje ta kasar Sin ta bayar, an ce, a yayin ziyarar ta kwanaki 4, Hu Jintao zai isa birnin Washington, kuma shugabannin kasashen biyu za su yi shawarwari kan batutuwan da suke fi daukar hankalinsu. Kuma Hu Jintao zai gana da manyan jami'an majalisar dokokin kasar Amurka, da yin mu'amala tare da bangarori daban daban. Daga baya, Hu Jintao zai kai ziyara birnin Chicago.

Bana shekara ce ta cika shekaru 40 da samun farfadowar dangantakar diplomasiyya a tsakanin kasashen biyu, bangarorin biyu sun mai da hankali sosai kan wannan ziyara. Bangaren Amurka ya bayyana cewa, zai yi matukar maraba da zuwan Mr. Hu Jintao, kuma za a shirya bikin maraba da liyafar karramawa ta kasa.(Abubakar)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China