in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hu Jintao ya gana da manema labaru na jaridun kasar Amurka
2011-01-17 16:45:01 cri
Ranar 18 ga wata, shugaban kasar Sin Hu Jintao zai tashi daga nan birnin Beijing domin kai ziyarar aiki a kasar Amurka. Litinin din nan 17 ga wata, kafin ya tashi, Hu Jintao ya yi magana da manema labaru na jaridar Wall Street ta Amurka da jaridar Washington Post ta Amurka, inda ya amsa tambayoyin da aka gabatar kan wasu batutuwa ciki har da habaka dangantaka a tsakanin kasashen biyu cikin dogon lokaci, kyautata halin da kamfanonin ketare ke ciki wajen zuba jari a kasar Sin, matakan da Sin ke dauka wajen tinkarar matsalar hada-hadar kudi, bunkasa kasar Sin cikin lumana, dangantakar dake tsakanin kasar Sin da kasashen kudu maso gabashin Asiya da halin da zirin Korea ke ciki da sauransu.

Game da dangantaka tsakanin kasashen biyu, Hu Jintao ya jaddada cewa, kasashen biyu na da bunkatun samun moriyar juna. Kamata ya yi, su kawar da duk wani shinge a tsakaninsu tare da kara bunkasa dangantakar dake tsakaninsu ta la'akari da moriyar jama'ar kasashen biyu da zaman lafiya duniya. Dadin dadawa, Hu ya ce, ko shakka babu, akwai wasu batutuwa masu daukar hankali a tsakaninsu, duk da hka, kamata ya yi, kasashen biyu su kara yin musayar ra'ayoyi da nuna amincewa da juna domin magance wadannan batutuwa yadda ya kamata ta yadda za a bunkasa dangantaka a tsakaninsu cikin lumana a dogon lokaci. Yayin da aka tabo batun amfani da dalar Amurka, Hu Jintao ya bayyana cewa, dala ta kasance muhimmiyar takardar kudi da ake amfani da ita a duniya, saboda haka, tsarin kudi na kasar Amurka yana yin babban tasiri kan kasuwannin kudi na duniya, ya kamata, ana ba da tabbaci ga tsarin yin amfani da dala. Ban da wanann kuma, game batun kudin Sin, Hu ya bayyana cewa, akwai abubuwa da dama da za a yi wajen mai da kudin Sin a matsayin kudin da za a iya yin amfani da shi a duniya ba tare da wani shinge ba.

Yayin da aka ambato batun halin da zirin Korea ke ciki, Hu Jintao ya bayyana cewa, a karkashin kokarin da kasar Sin da bangarori daban-daban suka yi, halin da ake ciki a zirin Korea ya sassauta. Sin tana fatan bangarorin da abin ya shafa za su yi amfani da zarafi mai kyau wajen farfado da shawarwari ta yadda za a kyautata halin da ake ciki a zirin.(Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China