in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Masanan Amurka na sa ran ziyarar da shugaban kasar Sin zai kai Amurka za ta kara amincewa da juna tsakanin kasashen biyu
2011-01-12 21:09:29 cri

Wani masani kan harkokin kasar Sin a jami'ar Johns Hopkins ta Amurka ya bayyana a kwanan baya cewa, yana sa ran ziyarar da shugaban kasar Sin Hu Jintao zai kai kasar Amurka nan gaba ba da jimawa ba za ta taimaka wajen kara samun amincewa da juna tsakanin kasashen biyu.

Masanin da ake kira Lanpton yana ganin cewa, ziyarar da shugaban kasar Sin zai kai Amurka tana da muhimmanci sosai, kuma wani babban burin da za a cimma wajen ziyara shi ne kara amincewa da juna tsakanin kasashen biyu, kana ma iya cewa haka ta cimma ruwa idan an cimma wannan buri.

Lanpton ya yi nuni da cewa, ziyarar da shugaban kasar Sin zai kai kasar Amurka ta shaida cewa, kasashen biyu sun gano moriya bai daya tsakaninsu, kuma ya kamata a tabbatar da hulda a tsakaninsu yadda ya kamata. Har wa yau, ya bayyana cewa, hadin gwiwar da ke tsakanin kasashen biyu ta bangaren tattalin arziki da ciniki ma ka iya kara samar da amincewa da juna tsakaninsu.(Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China