in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Laurent Gbagbo ya yarda da magance rikicin Cote D'ivoire ba tare da wani sharadi ba
2011-01-05 11:02:56 cri
Ranar 4 ga wata a Abuja babban birnin kasar Nijeriya, kungiyoyin AU da ECOWAS sun ba da sanarwa cikin hadin kai na cewa, shugaba Laurent Gbagbo ya amince da shawarar kungiyoyin biyu suka gabatar ba tare da wani sharadi ba domin magance rikicin siyasar kasa cikin lumana.

Sanarwar ta ce, ranar 3 ga wata, tawagar da ta hada firaministan kasar Kenya, shugabannin kasashen Benin, Saliyo, Cape Verd da shugaban kwamitin kungiyar ECOWAS ta isa Abidjan babban birnin kasar Cote D'ivoire domin shiga tsakanin matsalar kasar. Gbagbo ya nuna yarda wajen sulhunta wannan rikici ba tare da wani sharadi ba, kuma ya yi alkawari cewa, zai janye sojojin da ya jibga a waje da otel da tsohon firaministan kasar Ouattara ke ci.

Ban da wannan kuma, sanarwa ta ce, AU da ECOWAS sun sake jaddd goyon baya ga Ouattara a matsayin sabon shugaban kasar, kamata ya yi Gbagbo ya mikawa masa mulkin kasar tun da wuri. Dadin dadawa, sanarwa ta yi kira ga bangarori biyu na Ouattara da Gbagbo da su yi hakuri da juna domin hana tsanantar da halin da ake ciki.

An labarta cewa, ran 4 ga wata a Abuja, shugaban kasar Nijeriya dake rike da shugabancin karba-karba na ECOWAS Goodluck Jonathan ya jaddada cewa, idan Gbagbo bai mika iko ba ga Ouattara, to ECOWAS za ta dauki makakin soja bisa doka domin saukar da shi.(Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China