in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan kasar Kenya yana aikin shiga tsakani kan batun Cote D'ivoire
2011-01-03 10:09:03 cri
Ranar 2 ga wata, firaministan kasar Kenya Odinga ya tashi zuwa kasar Cote D'ivoire dake yammacin Afrika inda zai yi hadin kai tare da shugabannin kasashen Benin, Saliyo da Cape Verd domin kokarta warware rikici bayan babban zaben kasar.

Bisa labarin da ofishin firaminsitan kasar Kenya ya bayar, an ce, Odinga zai isa Abuja babban birnin kasar Nijeriya da farko domin tattaunawa kan yadda za a warware rikicin Cote D'ivoire tare da shugaban kungiyar ECOWAS kana da shugaban kasar Nijeriya Goodluck Jonathan. Daga baya, a matsayin wakilin neman sulhuntawa na kungiyar AU, Odinga zai je Cote D'ivoire domin shiga tsakani kan batun rikicin siyasar kasar tare da shugabannin kasashen Benin, Saliyo da Cape Verd.

An labarta cewa, a ran 27 ga watan Disamba na shekarar bara, AU ta nada Odinga a matsayin wakili a aikin shawo kan rikicin kasar Cote D'ivoire.(Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China