in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-moon ya yi kira da a warware matsalar siyasa ta kasar Cote d'Ivoire cikin lumana
2011-01-02 16:44:57 cri
Babban sakataren MDD Ban Ki-moon ya buga wayar tarho ga tsohon firaministan kasar Cote d'Ivoire Alassane Ouattara a ran 1 ga wata kan halin da kasar ke ciki yanzu, inda Ban Ki-moon ya jaddada cewa, ya kamata kasa da kasa su hada gwiwa, a kokarin samun wata hanya da ke dacewa wajen warware halin kaka-nika-yi da kasar Cote d'Ivoire ke ciki kwata kwata cikin lumana.

Haka kuma Ban Ki-moon ya furta cewa, ya dora matukar muhimmanci kan rahoton da aka bayar kan keta hakkin bil Adam a kasar Cote d'Ivoire. Kuma ya ba da umurni ga tawagar da ke gudanar da ayyuka da MDD ta tura zuwa kasar wato UNOCI wajen daukar matakai dadai karfinta domin shiga cikin yankunan da aka ambata a cikin rahoton, a kokarin hana da kuma binciken yadda ake keta hakkin bil Adam.

An shirya babban zabe a kasar Cote d'Ivoire a watan Nuwamba na shekara ta 2010, inda tsohon shugaban kasar Lauren Gbagbo da kuma Alassane Ouattara, shugaban jam'iyyar adawa kuma tsohon firaministan kasar dukkansu suka sanar da lashe zaben, da kuma kafa gwamnatocinsu, ko da yake MDD da kungiyar EU da ta AU sun nuna goyon baya ga Mr. Ouattara.(Kande Gao)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China