in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugabannin kasashe 3 na yammacin Afirka sun isa kasar Cote d'Ivoire don yin shiga-tsakani
2010-12-29 09:13:40 cri

A ran 28 ga wata, shugabannin kasashen Benin da Saliyo da Cape Verde sun isa birnin Abidjan dake kasar Cote d'Ivoire don neman kawo karshen mawuyacin halin siyasa da ake ciki a kasar bayan da aka kammala zaben shugaban kasar.

Shugabannin 3 sun yi shawarwari tare da wakilin musamman na babban sakataren MDD mai kula da harkokin kasar Cote d'Ivoire Choi Yong-jin da shugabannin kasar Cote d'Ivoire wato Gbagbo da Ouattara. Ya zuwa yanzu dai, ba a samu wani sakamako mai kyau kan shawarwarin ba.

A ran 2 ga wata, hukumar zaben kasar Cote d'Ivoire mai zaman kanta ta sanar da cewa, tsohon firaministan kasar Ouattara ya lashe zaben shugaban kasar. Kashe gari, kwamitin kundin tsarin mulkin kasar ya soke wannan sakamako, kana ya sanar da cewa, Gbagbo ya cimma nasara. A ran 4 ga wata, Gbagbo da Ouattara sun yi rantsuwar kama aiki bi da bi.(Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China