in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hukumar UNHRC ta yi suka ga aikin gallazawa da cin zarafin bil Adama da ke gudana a kasar Cote D'ivoire
2010-12-24 09:08:38 cri
A gun taron musamman a karo na 14 da hukumar UNHRC ta shirya a ran 23 ga wata a birnin Geneva, hukumar ta yi suka kau yanayin gallazawa da cin zarafin bil Adama da ke gudana a kasar Cote D'ivoire bayan babban zaben shugaban kasar, kuma ta yi kira ga bangarori daban daban da abin ya shafa da su dakafar da cin zarafin bil Adama.

A gun taron, mataimakiyar kwamishinan hukumar UNHRC Kyung-Wha Kang ta bayyana cewa, rukunin nazari kan hakkin bil Adam da M.D.D ta tura zuwa kasar Cote D'ivoire ya tabbatar da cewar yawan mutanen da suka mutu a sakamakon gallaza musu ya kai 173, an tsare mutane 471 a gidan kurkuku, kuma mutane 24 sun bace.

A ran 2 ga wata, hukumar babban zabe mai zaman kanta ta sanar da samun nasarar jam'iyyar adawa da gwamnatin da ke karkashin jagorancin tsohon firayim ministan kasar Ouattara a babban zaben. Kuma a ran 3 ga wata, kwamitin kula da tsarin mulkin kasar ya sanar da cewar tsohon shugaban kasar Gbagbo ya ci nasara a gun babban zaben. A ran 16 ga wata, an sheda fashin rikicin a tsakanin masu nuna goyon baya ga Ouattara da sojojin da ke karkashin jagorancin Gbagbo.(Abubakar)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China