in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An nuna maraba da kafa wani kwamitin binciken rikice-rikicen da suka faru bayan zabe a Cote D'ivoire
2010-12-22 16:10:08 cri

Ranar 21 ga wata, tsohon shugaban kasar Cote D'ivoire Laurent Gbagbo ya nuna maraba da kafa wani kwamitin binciken rikice-rikicen da suka faru bayan zaben shugaban kasa a Cote D'ivoire.

A wannan rana kuma, Laurent Gbagbo ya yi jawabi ta telibijin, inda ya nuna cewa, yana mutunta tsarin mulkin kasar da shari'a, kuma yana maraba da a kafa wannan kwamitin. Gbagbo ya ce, kwamitin zai dauki nauyin binciken ayyukan zabe da kokarin magance abkuwar wasu matsaloli cikin lumana.

Ban da wannan kuma, Gbagbo ya nuna cewa, kamata ya yi, kwamitin ya mai da wakilan wasu kungiyoyi ciki har da AU, ECOWAS, kungiyar kasashen dake amfani da kudin Cefa a Afrika, kungiyar tarayyar kasashen Larabawa, MDD, EU, Amurka, Rasha da Sin a matsayin rukunin ba da jagoranci.(Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China