in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-Moon ya yi Allah wadai da hare-haren da ake kaiwa sojojin kiyayen zaman lafiya na MDD a kasar Cote D'ivoire
2010-12-22 10:27:23 cri

Ranar 21 ga wata, babban sakataren MDD Ban Ki-Moon ya yi Allah wadai da hare-haren da magoyon tsohon shugaban kasar Cote D'ivoire Laurent Gbagbo ke kaiwa tawagar MDD dake kasar.

A wannan rana kuma, Ban Ki-Moon ya yi wa taron MDD bayyani kan halin da kasar ke ciki na cewa, ya nuna damuwa sosai ga batun an dakatar da samarwa tawagar wasu kayayyakin da suke bukata, kuma ya yi kira ga bangarorin da abin ya shafa da su yi kokarin ba da tallafi ga kungiyar.

A wannan rana a hedkwatar MDD, mataimakin sakatare mai kula da harkokin kiyaye zaman lafiya na majalisar Alain Le Roy ya bayyana cewa, yanzu Cote D'ivoire na cikin hali mafi tsanani. Bisa labarin da aka bayar an ce, magoyon Laurent Gbagbo sun fara kawo cikas ga ayyukan tawagar, alal misali, sun tilastawa wasu kamfanoni da su dakatar da samarwa tawagar kayayyakin da suke bukata tare da korar wasu ma'aikatan tawagar daga gidajensu da sauransu. Roy ya yi kira da su daina kai barazana ga ma'aikatan MDD.

An labarta cewa, ma'aikatar harkokin waje ta kasar Amurka ta sanar da hana shugaban kasar Cote D'ivoire Laurent Gbagbo da iyalansa shiga kasar Amurka a wannan rana.(Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China