in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-Moon ya nuna matukar damuwa ga tashe-tashen hankali a yankin Darfur na kasar Sudan
2010-12-22 10:24:11 cri
Ranar 21 ga wata, babban sakataren MDD Ban Ki-Moon ya ba da sanarwar nuna damuwa ga musayar wuta tsakanin sojojin gwamntin kasar Sudan da sashin Minawi na kungiyar 'yantar da Sudan a kwanan baya a yankin Darfur, kuma ya kalubalenci bangarorin biyu da su yi hakuri da juna tare da dakatar da kai farmaki.

Sanarwar ta ce, tashe-tashen hankali da bangarorin biyu suka tayar sun jawo asarar rayukan fararen hula da dukiya, kuma mutane da dama sun kaura daga wurarensu sannan kuma an tilasta wasu hukumomin jin kai da su bar wurin. Ban Ki-Moon kuma ya nuna matukar rashin jin dadi domin ganin cewa, an tada rikici a wani matsugunan 'yan gudun hijira dake yankin Shaeria.

Dadin dadawa, Ban Ki-Moon ya jaddada cikin sanarwar cewa, zai ci gaba da nuna goyon baya ga ayyukan da wasu kungiyoyi ciki har da sojojin kiyaye zaman lafiya na MDD da AU cikin hadin kai, hukumomin MDD, kungiyoyin masu zaman kansu suka yi a yankin.(Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China