in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin sulhu na MDD ya kalubalanci bangarori daban daban na Cote d'Ivoire da su yi iyakacin hakuri
2010-12-21 09:57:08 cri

A ran 20 ga wata, kwamitin sulhu na MDD ya ba da wata sanarwa, inda ya mai da hankali sosai kan jerin rikice-rikicen da aka samu a kasar Cote d'Ivoire, tare da kalubalantar bangarori daban daban na kasar da su yi iyakacin hakuri, a kokarin farfado da zaman lafiya da kwanciyar hankali a kasar.

A wannan rana, kwamitin sulhu ya yi wani taro kan yanayin da ake ciki a kasar Cote d'Ivoire, inda aka yanke shawarar tsawaita wa'adin kungiyar MDD a kasar zuwa ran 30 ga watan Yuni na badi. A sa'i daya, da babbar murya ne kwamitin sulhu ya yi Allah wadai da harin da aka kaiwa ma'aikatan kiyaye zaman lafiya na MDD a kasar Cote d'Ivoire a ran 18 ga wata, kuma ya yi gargadi cewa, za a yanke hukunci ga duk wadanda suka kai hari ga ma'aikatan kiyaye zaman lafiya na MDD da fararen hula.

A ran 2 ga wata, kwamitin harkokin zabe mai zaman kansa na Cote d'Ivoire ya sanar da cewa, shugaban kungiyar adawa Ouattara ya ci babban zaben shugaban kasar. A ran 3 ga wata, kwamitin kundin tsarin mulkin kasar Cote d'Ivoire ya shelanta cewa, shugaban kasar Laurent Gbagbo ya ci wannan zabe. Mutanen biyu sun yi rantsuwar kama aiki a ran 4 ga wata. Daga bisani, an fara yin rikice-rikice a kasar. MDD da kungiyar tarayyar Afirka da kungiyar tarayyar Turai suna nuna goyon baya ga Ouattara.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China