in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta musunta zargin da ake mata na bada tallafin makamai ga dakarun dake marawa Ouattara baya a kasar Cote D'ivoire
2010-12-20 19:10:42 cri

Ranar Lahadi 19 ga wata, dakarun Majalisar Dinkin Duniya dake kasar Cote D'ivoire sun musunta zargin cewa suna samar da tallafin makamai ga magoya bayan Alassane Ouattara.

Yayin da yake hira tare da manema labarai a wannan rana, kakakin dakarun MDD dake jibge a Cote D'ivoire ya ce, tawagarsa ba ta taba samar da goyon-bayan makamai ga duk wata kungiya ba, kuma tana nuna matsayinta na kasancewa tsaka-tsakiya.

Wannan kakaki ya kuma jaddada cewa, kungiyar MDD zata ci gaba da daukar nauyin shimfida zaman lafiya a kasar Cote D'ivoire, da nuna goyon-baya ga jama'ar kasar da su lalubo bakin zaren daidaita rikicin siyasar kasar yadda ya kamata.

Ranar 18 ga wata, Mista Laurent Gbagbo ya bada sanarwa ta kafar telebijin inda ya bukaci sojojin kasa da kasa da su janye daga kasarsa.(Murtala)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China