in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An ki yarda da duk wani yunkuri na neman kawo tsaiko ga matakan MDD a Cote d'Ivoire, in ji Ban Ki-moon
2010-12-18 17:11:33 cri
Babban sakataren MDD, Ban Ki-moon ya bayyana a ranar 17 ga wata a hedkwatar MDD da ke birnin New York cewa, ba za a yarda ba da duk wani yunkuri na neman kawo tsaiko ga matakan da MDD ke dauka a kasar Cote d'Ivoire.

A gun taron manema labarai da aka yi a wannan rana, Ban Ki-moon ya ce, aikin gaggawa yanzu shi ne a hana ayyukan da za su iya kara tsananta halin da ake ciki a kasar Cote d'Ioivre. Tuni ECOWAS da AU sun bayyana matsayinsu na girmama wa tsarin mulkin kasar da burin jama'a, kuma abin da MDD ke son bayyana shi ne, sakamakon zabe ya bayyana kome, babu sauran hanyoyin da za a iya zaba.

Sa'an nan, Ban Ki-moon ya matsa wa Laurent Gbagbo kaimin sauka daga karagar mulki tare kuma da mika mulki ga abokin hamayyarsa.

Har wa yau, a ranar 17 ga wata, majalisar gudanarwa ta Amurka ta ce, abu ne na haram da Gbagbo ya ci gaba da rike da ragamar mulki, idan har ya ki sauka daga mukaminsa, lallai, Amurka na shirin kakaba takunkumi gare shi tare kuma da magoya bayansa.(Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China