in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Zanga-zangar da aka yi a kasar Cote d'Ivoire ta haddasa rikici mai tsanani
2010-12-17 15:18:56 cri

A ran 16 ga wata, a Abidjan, hedkwatar tattalin arzikin kasar Cote d'Ivoire, masu nuna goyon baya ga Alassane Dramane Ouattara shugaban jam'iyyar adawa da gwamnatin kasar sun yi zanga-zanga a wasu wurare a birnin, kuma an samu rikicin tsakanin masu zanga-zanga da sojojin tsaron kasar da ke karkashin jagorancin shugaban kasar Laurent Gbagbo, al'amarin da ya yi sanadiyar mutuwar mutane fiye da 10. Wasu masu nazarin lamuran yau da kullum sun yi hasashen cewar mai yiyuwa ne rikicin da aka samu a birnin Abidjan zai haddasa yakin bassasa a kasar, kuma ya kamata kasashen duniya su dauki matakai daban daban don sassauta halin da kasar Cote d'Ivoire take ciki, domin kaucewa tashe-tashen hankali a kasar.

A ran 31 ga watan Nuwanba, kasar Cote d'ivoire ta gudanar da babban zaben shugaban kasar a zagaye na biyu. Kwamitin kula da babban zaben mai zaman kansa ya sanar da cewar shugaban jam'iyyar adawa da gwamnatin kasar kuma tsohon firayim ministan kasar Alassane Dramane Ouattara ya ci nasara, kuma M.D.D da kungiyar AU da kungiyar ECOWAS sun nuna goyon baya ga sanarwar da kwamitin ya bayar. Amma, a ran 1 ga wata, kwamitin kula da tsarin mulkin kasar Cote d'ivoire ya ki amincewa sanarwar da kwamitin ya bayar, kuma ya sanar da cewar shugaban kasar Laurent Gbagbo ya ci nasara. Saboda haka, Laurent Gbagbo da Alassane Dramane Ouattara kowa daga wajensa ya ce shi ya samu nasara, kuma sun kafa gwamnatinsu bi da bi, ta haka, kasar ta kasance da shugabanni 2.

1 2
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China