in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Da kyar za a iya kawar da mawuyacin halin dake ciki a kasar Kodivwa
2010-12-16 16:01:28 cri
A ranar 15 ga wata, babban sakataren MDD, Ban Ki-Moon ya bayar da wata sanarwa, inda ya nuna damuwa ga matsanancin hali da kasar Kodivwa ke ciki ta fuskar siyasa, kuma ya kalubalanci bangarori daban daban na kasar da su yi hakuri da juna don magance abkuwar yakin basasa.

A cikin sanarwar kuma, Ban Ki-Moon ya kara yin kira ga Laurent Gbagbo da ya  girmama ra'ayin jama'ar kasar, da kuma mika mulki ga Alassane Ouattara da ya ci zaben shugaban kasar. Dadin dadawa, ya yi kira ga bangarori daban daban da abin ya shafa da su yi mu'ammala tare da shugabannin shiyya-shiyya da na kasa da kasa, don kawar da rikicin siyasa ta hanyar lumana.

Ana ta kara samun tsanancewar yanayi a kasar Kodivwa sakamakon shugabanni biyu da kowanne ke ikirrarin kasancewa shugaba a kasar. Tawagar MDD dake kasar ta bayyana cewa, rundunar sojojin kiyaye zaman lafiya ta kara sintiri a sama da kasa, don tabbatar da tsaron kasar.

A ran 2 ga wata, hukumar zabe mai zaman kanta ta kasar Kodivwa ta sanar da cewa, tsohon firaministan kasar, Alassane Ouattara a matsayin wanda ya ci zaben shugaban kasar. Amma a ranar 3 ga wata, kwamitin tsarin mulkin kasar ya sanar da soke sakamakon da hukuma ta bayar, kana ya ce, shugaban kasar na yanzu Laurent Gbagbo ya lashe zaben. A ranar 4 ga wata, mutanen biyu sun yi rantsuwar kama aiki daya bayan daya, a ranar 5 ga wata kuma, dukkansu sun sanar da sunayen ministocin sabbin gwamnatocinsu, al'amarin da ya janyo wani kace-nace. MDD, da kungiyar AU, da kungiyar EU, da kuma sauran kungiyoyin duniya sun nuna goyon baya ga Alassane Ouattara.

1 2
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China