in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar AU ta ki yarda da sanya wa Cote D'ivoire takunkumi
2010-12-13 14:13:25 cri

Ranar 12 ga wata, jami'in kula da harkokin zaman lafiya da tsaro na kungiyar tarrayar kasashen Afrika wato AU Ramtane Lamamra ya ce, AU tana fatan a dauki wani matakin diplomasiyya mai amfani da zai shawo kan matsalar Cote D'ivoire a maimakon sanya mata takunkumi.

A gun wani taron daidaita batun rigingimu a kasashen Afrika na AU da aka yi a birnin Algiers, Lamamra ya ce, AU tana ci gaba da dukufa kan fitar da wani matakin maido da dimokuradiyya da zaman lafiya a Cote D'ivoire. Kuma AU ta amince da nasarar tsohon firaministan kasar kuma shugaban jam'iyyar RDR Alassane Ouattara a zaben shugaban kasar, kuma ta yanke shawarar dakatar da Cote D'ivoire daga kungiyar AU cikin gajeren lokaci.

An labarta cewa, a ran 28 ga watan Nuwamba, Cote D'ivoire ta kada kuri'ar zaben shugaban kasa zagaye na biyu. Kuma a ran 2 ga wata, kwamitin zabe mai zaman kansa ya sanar da Ouattara a matsayin wanda ya lashe zabe da kashi 54.1 bisa 100, amma a ranar 3 ga wata, kwamitin tsarin mulkin kasar ya sanar da Laurent Gbagbo shugaban kasar mai ci a matsayin wanda ya lashe zaben da kashi 51.45 cikin 100. A ranar 4 ga wata, mutanen biyu sun yi rantsuwar kama aiki a matsayin shugaban kasar, hakan ya hadasa hadarin siyasa mai tsamani a kasar.(Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China