Kakakin ma'aikatar harkokin waje ta kasar Philip J. Crowley ya bayyana cewa, gwamnatin kasar Amurka ta riga ta mika wata wasikar da shugaban kasar Barack Obama ya rubuta zuwa ga shugaban kasar Cote d'Ivoire na yanzu Laurent Gbagbo, inda ya ce, idan Gbagbo ya yi kuskure, kasarsa za ta fuskanci rikici mai tsanani.(Zainab)