in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar AU ta dakatar da kasar Cote d'Ivoire
2010-12-10 10:34:21 cri
A ran 9 ga wata a birnin Addis Ababa, majalisar kula da harkokin zaman lafiya da tsaro ta kungiyar tarayyar Afirka wato AU ta gudanar da taron musamman game da rikicin siyasar kasar Cote d'Ivoire, kungiyar ta tsaida kudurin dakatar da kasar.

A cikin sanarwar da aka bayar bayan taron, an ce, kungiyar AU za ta ci gaba da neman hanyoyin warware rikicin siyasa na kasar Cote d'Ivoire cikin lumana bisa kudurin da aka tsaida.

Ban da wannan kuma, sanarwar ta kalubalanci tsohon shugaban kasar Cote d'Ivoire Laurent Gbagbo da ya dora muhimmanci kan moriyar kasarsa har ma a nahiyar Afirka, da girmama sakamakon zaben, da kuma mika iko ga tsohon firaministan kasar Alassane Ouattara ba tare da bata lokaci ba.(Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China