in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
ECOWAS ta dakatar da kasar Cote d'Ivoire daga cikin kungiyar
2010-12-08 09:07:18 cri
A ran 7 ga wata a birnin Abuja, hedkwatar kasar Nijeriya, shugaban gudanarwa na taron ministocin gamayyar tattalin arziki ta kasashen yammacin Afirka(ECOWAS), kana shugaban kasar Nijeriya Goodluck Jonathan ya shelanta cewa, kungiyar ECOWAS ta yanke shawarar dakatar da kasar Cote d'Ivoire daga cikin kungiyar, a kokarin nuna goyon baya ga shugaban jam'iyyar adawa, kana tsohon firaministan kasar, Alassane Dramane Ouattara a matsayin shugaban kasar.

Goodluck Jonathan ya fadi haka bayan da ya yi shawarwari da takwarorinsa na Senegal, Togo, Ghana, Liberiya, Burkina Faso, da kuma tsohon shugaban kasar Mali.

A wannan rana, shugabannin kasashe 7 na kungiyar ECOWAS sun fitar da wata sanarwa bayan sun kira taron gaggawa. A karshe shugabannin sun jaddada goyon bayansu ga Ouattara a matsayin sabon shugaban kasar Cote d'Ivoire, tare da matsa lamba ga shugaban kasar Laurent Gbagbo da ya amince da sakamakon zabe zagaye na biyu ta hanyar mika mulkin kasar tun da wuri.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China