in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-Moon na nuna damuwa ga yanayin siyasa da Kodivwa ke ciki
2010-12-05 17:00:46 cri
Babban sakataren MDD Ban Ki-Moon ya bayar da sanarwa ta bakin kakakinsa a ranar 4 ga wata, inda ya bayyana cewa, ko da yake kwamitin zabe mai zaman kansa na kasar Kodivwa ya sanar da sakamakon zaben shugaba na zagaye na biyu da aka amince da shi a ranar 2 ga wata, amma har zuwa yanzu kasar na cikin mawuyacin hali ta fuskar siyasa.

Bayan haka kuma, Ban Ki-Moon ya kara yin kira ga jama'ar kasar da su tabbatar da samun natsuwa da kwanciyar hankali, kana kuma ya jaddada cewa, kungiyar musamman ta MDD dake kasar Kodivwa za ta yi iyakacin kokari bisa iznin da ta samu don tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a kasar.

A ranar 4 ga wata a fadar shugaban kasar Kodivwa, shugaban kasar, Laurent Gbagbo ya yi rantsuwar kama aikinsa na sabon shugaban kasar. Amma, bayan haka ba da dadewa ba, 'dan dakara daban, kuma tsohon firaministan kasar, Alassane Ouattara shi ma ya yi rantsuwar hawan kujerar mulkin kasar. A ranar 3 ga wata, kwamitin kula da tsarin mulki na kasar Kodivwa ya sanar da cewa, Laurent Gbagbo ya samu nasara bisa kuri'un da ya samu na kashi 51.45 cikin kashi 100, har ma ya soke sakamakon da kwamitin zabe mai zaman kansa na kasar ya sanar a ranar 2 ga wata game da Alassane Ouattara ya samu nasara bisa kuri'un da ya samu na kashi 54.1 cikin kashi 100. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China