in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An fara zaben shugaban kasar Cote d'Ivoire zagaye na biyu yadda ya kamata
2010-11-29 09:37:08 cri

A ran 28 ga wata, aka gudanar da zaben shugaban kasar Cote d'Ivoire zagaye na biyu a tasoshin  zabe dubu 20 a dukkan kasar. An fara zaben karfe 7 da safe tare da kammala shi karfe 5 da yamma yadda ya kamata.

Duk da cewa akwai wasu tasoshin jefa kuri'un da ba su bude cikin lokaci ba, amma an gudanar da zaben shugaban kasar yadda ya kamata. An ce yawan mutane da suka jefa kuri'u a zagaye na biyu ya ragu sosai bisa na zagayen farko.

'Yan takaran biyu na zaben shugaban kasar a zagaye na biyu wato tsohon firaministan kasar Alassane Dramane Ouattara da shugaban kasar na yanzu Laurent Gbagbo sun jefa kuri'a a wata mazaba dake birnin Abidjan, babban birnin kasar. Bayan da suka jefa kuri'a, sun bayyana cewa, suna da imanin cin nasara. Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasar za ta bada sakamakon zaben a cikin kwanaki 3 masu zuwa.(Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China