in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta kara saurin gina hanyoyin mota a yankunan karkara
2010-11-22 16:39:24 cri
Ibrahim: A ran 26 ga watan Oktoban da ya wuce, an kaddamar da layin dogo mai saurin tafiya wanda zai rika sintiri a tsakanin biranen Shanghai da na Hangzhou dake gabashin kasar Sin, jirage suna tafiyar da sun kai kilomita 350 cikin sa'a daya. A cikin 'yan shekarun da suka gabata, bayan da aka kara saurin shimfida layin dogo mai saurin tafiya a tsakanin manyan biranen kasar Sin, mazauna birane suna samun saukin tafiye-tafiye a tsakanin biranen kasar. Amma ga dimbin manoma wadanda yawansu ya kai miliyan dari 9 kuma suke zaune a yankunan karkara, sabo da gidajensu suna da nisa da irin wadannan hanyoyin jiragen kasa na zamani, ko za su iya samun saukin yin balaguro? Wannan shi ne batun da ake nazari a kai a kasar Sin. Mr. Liu Wenjie, babban sakataren kungiyar nazarin ilmin hanyar mota ta kasar Sin ya bayyana cewa, "Layin dogo mai saurin tafiya wani sabon abu ne dake jawo hankalin mutane sosai, amma a ganina, ya kamata a yi la'akari da wasu abubuwa. Yanzu ba a ambaton hanyoyin mota na yankunan karkara, kuma ba a iya rabuwa da su. Hanyoyin mota sun kasance tamkar kananan hanyoyin jini dake jikin dan Adam sabo da suna hade da iyalai da kauyuka daban daban. Sakamakon haka, hanyoyin mota na yankunan karkara sun fi muhimmanci a idon manoma."

Sanusi: Ko da yake yanzu ba a ambaton hanyoyin mota na yankunna karkara ba, amma gaskiyar magana ita ce a cikin shekaru da yawa da suka wuce, an samu ci gaba sosai wajen shimfida hanyoyin mota a yankunan karkara. A gun wani taro mai nasaba da batun hanyoyin mota na yankunan karkara, da aka yi a lardin Shandong a kwanan baya, Mr. Feng Zhenglin, mataimakin ministan ma'aikatar zirga-zirga ta kasar Sin ya bayyana wa mahalarta taron fiye da dari 4 halin da ake ciki, cewar "Gwamnatin kasar Sin na mai da hankali sosai kan aikin gina hanyoyin mota a yankunan karkara. Bisa kokarin da ta yi cikin shekaru da yawa da suka gabata, hanyoyin mota da aka gina a yankunan karkara sun samu kyautatuwa. An yi hasashen cewa, ya zuwa karshen bana, tsawonsu zai kai kilomita miliyan 3 da dubu 450. Haka kuma, hanyoyin mota na yankunan karkara sun taka muhimmiyar rawa wajen zamanintar da yankunan karkara da kara yawan kudin shiga da manoma suke samu. Sakamakon haka, sun kasance wata muhimmiyar kafa dake zamintar da yankunan karkara na kasar Sin."

Ibrahim: Bisa kididdigar da aka yi, an ce, ya zuwa karshen shekarar 2009, tsawon hanyoyin mota da aka gina a yankunan karkara na kasar Sin ya kai fiye da kilomita miliyan 3 da dubu dari 3 wadanda suke hade da kusan dukkan kananan garuruwan dake yankunan karkara. Amma a shekarar 1978, jimillar tsawonsu kimanin kilomita dubu 586 ne kawai, kuma babu hanyar mota ko da kilomita daya a yawancin kananan garuruwan dake yankunan karkara.

Sanusi: Ci gaban da kasar Sin ta samu a fannin gina hanyoyin mota a yankunan karkara ya jawo hankalin gamayyar kasa da kasa sosai. Sabili da haka, kawancen kungiyoyin kula da hanyoyin mota ta kasa da kasa ta bai wa ma'aikatar zirga-zirga ta kasar Sin lambar yabo ta samar da "hanyoyin mota na yankunan karkara da adalcin dake kasancewa a zaman al'umma" domin yabawa kasar Sin sabo da kyakkyawan sakamako da ta samu wajen gina hanyoyin mota a yankunan karkara. Mr. Kapila, shugaban wannan kawance ya kuma yaba wa kokarin da kasar Sin ta yi wajen gina hanyoyin mota a yankunan karkara, inda ya ce, "Kasar Sin ta samu kyakkyawan sakamako sosai wajen gina hanyoyin mota, musamman a yankunan karkara. Ina fatan za ta ci gaba da yin haka a nan gaba."

Ibrahim: Shi kuma, Mr. Kabila yana ganin cewa, hanyoyin mota da aka gina a yankunan karkara sun taka muhimmiyar rawa wajen magance matsalar talauci a kasar Sin. Yana fatan sauran kasashe masu tasowa su yi koyi da kasar Sin wajen gina hanyoyin mota a yankunan karkara domin kyautata rayuwar manoma.

Sanusi: Ko da yake kasar Sin ta samu ci gaba sosai wajen gina hanyoyin mota a yankunan karkara, amma kuma tana fuskantar kalubale sosai, sabo da ba a samu daidaito a tsakanin yankuna daban daban wajen neman ci gaba, kuma jama'a ba su san yadda za su iya kare hanyoyin mota daga lalacewa ba, har ma ba a san yadda za a iya kulawa da hanyoyin mota dake yankunan karkara ba. Game da wadannan kalubale, Mr. Niu Jiatang, shugaban hukumar zirga-zirga ta birnin Zaozhuang ya ce, "Kulawa da hanyoyin mota dake yankunan karkara hakki ne na jama'a. Lokacin da yawancin jama'a ba su san yadda za su kiyaye su ba, dole ne gwamnati ta ba da jagoranci. Sabo da haka, gwamnatin lardin Shandong ta kebe wasu kudi domin kiyaye ingancin hanyoyin mota na yankunan karkara musamman." (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China