in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babban manajan kamfanin gina gadoji da hanyoyi na kasar Sin na fatan karfafa zumunci tsakanin Sin da Afirka
2010-11-11 16:42:05 cri
A halin yanzu, ana kokarin gudanar da wani aiki na fidda manyan kamfanonin kasar Sin 10 wadanda suka bayar da babbar gudummawa ga karfafa dankon zumuncin tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka, wanda kungiyar sada zumunci tsakanin jama'ar kasashen Sin da Afirka da gidan rediyon CRI suka dauki nauyin shiryawa. Babban manajan kamfanin kula da ayyukan gina gadoji da hanyoyi na kasar Sin, wanda shi ne daya daga cikin kamfanonin da suka tsaya takara a wannan karo, Mista Wen Gang ya kawo ziyara nan gidan rediyon CRI a ranar 10 ga wata, inda ya bayyana abin da ya sani a game da nahiyar Afirka.

Mista Wen Gang ya ce, a kasashen Afirka da dama, ana iya ganin gadoji da hanyoyin da kasar Sin ta gina, kuma ma'aikata Sinawa suna nuna kwazo wajen gina muhimman ayyukan biyan bukatun jama'a a kasashen Afirka, ciki kuwa har da shimfida hanyoyi, gina gadoji da sauransu. Ya zuwa yanzu, ma'aikatan kasar Sin sun shafe tsawon shekaru sama da 50 suna kokarin bada taimako wajen gina gadoji da hanyoyi a nahiyar Afirka. Mista Wen ya kuma waiwayi wahalhalun da Sinawa suka fuskanta yayin da suke kokarin raya sana'o'insu a kasashen Afirka, da bayyana yadda kamfanonin kasar Sin suka samu bunkasuwa a wurin, gami da manyan sauye-sauyen da nahiyar Afirka ta samu a sabon halin da ake ciki.

Mista Wen Gang ya ce, yana fatan gadoji da hanyoyin da kasar Sin ta gina a kasashen Afirka za su kasance tamkar wata babbar gada dake sada zumunta tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka, a kokarin bayar da gudummawa ga mu'amala da ci gabansu.(Murtala)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China