in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta sanar da rahoto kan huldar da ke tsakaninta da kasashen Afirka ta fuskar tattalin arziki da cinikayya a shekarar 2010
2010-10-14 17:27:40 cri
Cibiyar binciken hadin gwiwar kasa da kasa ta fuskar cinikayya da tattalin arziki da ke karkashin laimar ma'aikatar kasuwancin kasar Sin ta sanar da wani rahoto kan yadda ake kokarin kyautata huldar da ke tsakaninta da kasashen Afirka ta fuskar tattalin arziki da cinikayya a shekarar 2010, a ranar 14 ga wata a nan birnin Beijing, rahoton ya bayyana irin nasarorin da kasar Sin da kasashen Afirka suka samu a shekarun baya a fannonin tattalin arziki da cinikayya, da zuba jari, da makamantansu.

Rahoton da aka bayar ya shaida cewa, zuwa karshen shekarar bara, yawan kudin kayayyakin da ake cinikayyar a tsakanin Sin da Afirka ya zarce dala biliyan 91, hakan ya sa kasar Sin ta zama kawar kasashen Afirka wadda ta fi yin ciniki da su. Haka kuma yawan jarin da kasar Sin ta zuba a Afirka kai tsaye, da jarin da kasashen Afirka suka zuba kasar Sin, dukkansu sun kai kimanin dala biliyan 10. Ban da haka kuma, kasashe fiye da 50 ne suka amfana da tallafin da kasar Sin ta baiwa Afirka, hade da ayyuka fiye da 800, kuma wannan tallafi ya shafi bangaren gidaje, noma, aikin adana ruwa, sadarwa, zirga-zirga, jinya, da dai sauran fannoni daban daban.

Sa'an nan rahoton ya kara bayyana cewa, a nan gaba, Sin da Afirka za su yi kokarin habaka hadin kan da ke tsakaninsu zuwa wasu sabbin fannoni kamarsu hada-hadar kudi, masana'antu, yawon shakatawa, zirga-zirgar jiragen sama, da makamantansu. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China