in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 14 sun rasa rayukansu sakamakon fashewar boma-bomai a Abuja
2010-10-02 17:04:06 cri
A ranar 1 ga wata, an samu fashewar boma-bomai da aka dasa a motoci har sau biyu a Abuja, babban birnin kasar Nijeriya, sakamakon haka, mutane 14 sun rasa rayukansu, yayin da mutane fiye da 40 suka ji rauni.

Bangaren 'yan sanda na kasar Nijeriya ya ce, an samu wannan fashewar boma-bomai ne a kusa da wurin shirya aikace-aikace game da bikin murnar cika shekaru 50 da Nijeriya ta samu 'yanci daga Turawan mulkin mallaka na kasar Burtaniya. Amma, ba a dakatar da bikin ba sakamakon lamarin.

Bayan abkuwar lamarin, kungiyar neman hakkin yankin Niger Delta ta kasar Nijeriya, wato MEND ta yi shelar daukan alhakin lamarin, ta kuma bayyana cewa, sun yi haka ne don nuna adawa da bikin.

Yanzu, mutanen da suka ji rauni suna samun jinya a asibiti. Bangaren 'yan sanda kuma yana bincike kan lamarin. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China