in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi bikin ranar rumfar kasar Afrika ta tsakiya a yayin bikin Expo na Shanghai
2010-09-25 21:07:13 cri

A ranar 25 ga watan Satumba, an yi bikin ranar rumfar kasar Afrika ta takiya a yayin bikin Expo na Shanghai. Shugaban hukumar kula da harkokin kasuwanci da masana'antu ta kasar Sin Mr. Zhou Bohua da shugaban kasar Afrika ta tsakiya François Bozizé Yangouvonda da ministar kula da harkokin kasuwanci ta kasar Emilie Beatrice Epaye da manyan jami'an gwamnatocin kasashen biyu da mutane a harkokin kasuwanci sun halarci wannan biki tare.

A cikin jawabin fatan alheri da Mr. Zhou Bohua ya yi, ya bayyana cewa, a cikin 'yan shekarun nan, a karkashin kokarin bangarorin biyu, dangantakar kasashen biyu ta kara bunkasa cikin hanzari, kuma hadin gwiwa a fannin tattalin arziki da cinikayya da ke tsakaninsu ta samu sakamako mai gamsarwa. Yana fata za a yi amfani da bikin Expo na Shanghai, domin kara fahimtar juna da koyon fasahohi da sada zumunci da ke tsakaninsu, don kara inganta dangantakar hadin gwiwa ta sada zumunci da ke tsakaninsu.

Emilie Beatrice Epaye ta yi jawabin fatan alheri, inda ta bayyana cewa, a cikin 'yan shekarun nan, kasar Afrika ta tsakiya na yin gyare-gyare da dama, kuma tana fatan yin amfani da wadannan gyare-gyare don kawo wani kyakkyawan muhallin zuba jari ga masu zuba jari na kasashen waje, haka kuma, kasar Afrika ta tsakiya za ta yi amfani da bikin Expo na Shanghai, don inganta hadin gwiwa da ke tsakaninta da kasar Sin, da inganta dangantakar hadin gwiwa ta sada zumunci da ke tsakaninsu.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China