in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hadin gwiwar tattalin arziki da ciniki a tsakanin kasar Sin da kasashen Afrika ya kawo moriyar bangarorin biyu
2010-09-14 15:52:05 cri

"Hadin gwiwar tattalin arziki da ciniki a tsakanin kasar Sin da kasashen Afrika ya kawo moriyarsu", "kasashen Afrika suna bukatar kasar Sin, kuma kasar Sin ta mai da kasashen Afrika a matsayin abokanta", wakilinmu ya kan ji ana tabo wannan zance a gun taron kara wa juna sani a kasar Faransa.

Kwararru da masana da 'yan kasuwa fiye da dari daya da suka fito daga kasashen Faransa da Sin da kasashen Afrika sun halarci wannan taro. Darektan ofishin nazarin bunkasuwa na bankin raya Afrika na ganin cewa, nahiyar Afrika tana fuskantar gyare-gyare da yawa, ya kamata kasashen Afrika su kara yin kokarin raya tattalin arziki amma ba kubutar da kangin talauci kawai ba, sabo da haka, kasashen Afrika suna bukatar kawa kamar kasar Sin. Ya ce, "kasar Sin ta zuba jari a kasashen Afrika, kana kasar Sin ta nuna kwarewa wajen raya tattalin arziki, hadin gwiwa a tsakaninsu ya kawo moriyar juna."

1 2 3
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China