in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Matsakaita da kananan kamfanonin kasar Sin suna yin kokari wajen yin ciniki tare da kasashen Afirka
2010-09-13 15:00:23 cri

Tun daga ran 8 ga wata zuwa ran 11, an gudanar da taron tattaunawar zuba jari da cinikayya na kasa da kasa a birnin Xiamen na lardin Fujian da ke kudancin kasar Sin, 'yan kasuwa fiye da dubu 50 da ke zuwa daga kasashe kimanin 100 sun halarci taron. A ganin manema labaru na gidan rediyon kasar Sin, sabo da ana kyautata yanayin zuba jari na kasashen Afirka, matsakaita da kananan kamfanonin kasar Sin suna yin kokari wajen yin ciniki tare da kamfanonin kasashen Afirka.

Shugaban kamfani mai suna "Ke Duo Wei" na birnin Shenzhen Hui Honglin yana daya daga cikin shugabannin matsakaita da kananan kamfanonin kasar Sin da ke yin ciniki tare da kamfanonin kasashen Afirka. A shekarar 2001, Hui Honglin tare da abokansa sun tara kudin Sin RMB miliyan daya, kuma sun kafa kamfani kansu, wannan kanfani yana kula da harkokin fitar da kayayyakin sake-sake zuwa kasashen Afirka. Amma kamfanin ya taba fuskantar kalubale da yawa.Hui Honglin ya bayyana cewa: "muhimmin kalubalen da muke fuskantar shi ne rashin kudi, kuma a ganina akwai wuya ga kasar da ta nuna goyon baya ga kananan kamfanoni."

1 2 3
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China