in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi shagalin ranar rumfar Nijeriya a bikin baje kolin kasa da kasa na Shanghai
2010-08-21 16:40:10 cri

A Asabar 21 ga watan Agusta. Manyan jami'an dake halartar bikin sun hada da Jubril Martins-Kuye, ministan kasuwanci da masana'antu na kasar Nijeriya, da Wang Yongqiu, tsohon jakadan kasar Sin a Nijeriya.

A jawabin da sanata Jubril Martins-Kuye ya gabatar, ya yi bayani kan irin dimbin albarkatun kasa da Allah ya hore wa kasar Nijeriya, da kuma yadda gwamnatin kasar take kokarin bunkasa bangarori daban daban da nufin kara janyo masu zuba jari zuwa kasar. A sa'i daya kuma, sanata Kuye ya nuna yabo kan bikin EXPO na Shanghai tare da bayyana cewa, zuwansa bikin Expo zai taimakawa Nijeriya ta karu da fasahohi da yawa musamman ma ta fuskar kiyaye tsarin birane da kyautata muhalli, sa'an nan shagalin rumfar kasar da ake yi zai baiwa wasu kasashe karin damar fahimtar Nijeriya ta fannin ci gaban tattalin arziki da siyasa.

A nasa jawabin, jakada Wang Yongqiu ya bayyana kyakkyawar dangantakar da ke tsakanin kasashen 2. Haka kuma ya bayyana imaninsa game da yadda kasashen 2 za su yi amfani da damar da bikin ya samar wajen habaka hadin gwiwarsu a fannoni da dama.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China