Idan tsohon shugaban kasar Mandela zai halarci gasar karshen da za a gudanar a filin wasan kwallon kafa mai suna FNB, mai yiyuwa ya mika kofin duniya ga kungiyar da ta zama zakara. Amma bisa labarin da kakakin hukumar FIFA ya bayar, an ce, ba a tabbatar da Mandela zai halarci gasar karshen ba.
A cikin wata sanarwa da asusun Mandela ya bayar, an tabbatar da cewa, Mandela ya riga ya sami takardar gayyatar da hukumar FIFA ta bayar, amma Mandela zai yanke shawarar ko zai halarci gasar karshe a ran da za a gudanar da gasar.(Abubakar)