in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An taya murnar ranar rumfar kasar Rwanda a bikin EXPO na Shanghai
2010-07-04 14:56:00 cri
Yau 4 ga watan Yuli da safe, an shirya bikin murnar ranar rumfar kasar Rwanda a yayin bikin EXPO na Shanghai. Firayin minista Bernard Makuza na kasar Rwanda da Mr. Li Rongrong, shugaban kwamitin sa ido kan kadaron kasar Sin, sun halarci biki a madadin gwamnatocin kasashen Rwanda da kasar Sin, kuma bi da bi, sun bayar da jawabai.

A cikin nasa jawabi, Mr. Bernard Makuza ya ce, "Yau ina farin cikin halartar wannan bikin murnar ranar rumfar kasar Rwanda da aka shirya a yayin EXPO na Shanghai. Da farko dai, na wakilci shugaban kasarmu Paul Kagame da dukkan jama'ar kasar Rwanda, na nuna gaisuwa cikin sahihanci ga shugaba da jama'ar kasar Sin."

Sannan Mr. Makuza ya ce, ko da yake ban dade ina nan kasar Sin ba, amma na riga na san nasarar da kasar Sin, musamman jama'ar birnin Shanghai, suka samu wajen shirya bikin EXPO na shekara ta 2010. Mr. Makuza ya kuma nuna godiya ga gwamnatin kasar Sin da ta taimaki kasar Rwanda da sauran kasashen Afirka wajen halartar bikin EXPO na Shanghai.

Bayan bikin murna, mawaka da 'yan kada ganga na kasar Rwanda sun rera wa mahalarta wasu wakoki da kuma taka raye-raye. Yau da dare, za su kuma nuna wasu wasannin kwaikwayo ga masu yawon bude ido na kasar Sin. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China