in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hu Jintao ya halarci taron matakin farko na taron koli na G20
2010-06-27 21:53:19 cri

An fara shirya taro na matakin farko na taron shugabannin kasashe mambobin kungiyar G20 da misalin karfe 9 na safe a ranar 27 ga wata bisa agogon Toronto, inda ake karbar bakuncin taron. A wajen taron kuma, shugaba Hu Jintao na kasar Sin ya gabatar da muhimmin jawabi mai taken 'yin kokari tare don samar da makoma mai kyau a nan gaba', haka kuma ya bayyana ra'ayin kasar Sin dagane da yanayin da tattalin arzikin duniya ke ciki, da neman yin kwaskwarima ga asusun ba da lamuni na duniya wato IMF, hade da yin kira da a kara mai da hankali kan batun ci gaba.

Kamar yadda aka tanada, shugabannin kasashe daban daban za su tofa albarkacin bakinsu daya bayan daya dangane da babban taken taron na 'farfadowa da sabon mafari', inda shugaba Hu Jintao zai zama na biyu wajen gabatar da jawabi. Kafin haka kuma, Hu ya yi nuni da cewa, game da taron da ake yi kasar Sin na da bukatu 4, wadanda suka hada da kara yin mu'amala kan manyan tsare-tsaren tattalin arziki don tabbatar da farfadowar tattalin arzikin duniya, da yin kokarin gyara tsarin hukumar IMF don kara yin wakilci ga kasashe masu tasowa, da kara mai da hanakli kan batun ci gaba, gami da yin kokarin kau da matakan kariyar ciniki iri daban daban. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China