in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaba Hu Jintao ya gana da takwarorinsa na kasashen Amurka da Rasha, kana da firaministan kasar Birtaniya
2010-06-27 16:14:38 cri

A ran 26 ga wata da yamma bisa agogon birnin Toronto na kasar Canada, shugaba Hu Jintao na kasar Sin ya gana da takwaransa na kasar Amurka Barack Obama, inda shugaba Hu ya bayyana cewa, yanzu yanayi mai sarkakiya da duniya ke ciki yana samun sauyawa, Sin da Amurka suna tinkarar kalubale baki daya. Ya kamata su ci gaba da inganta hadin kansu domin moriyar juna. Haka kuma shugaba Hu ya amince da gayyatar da shugaba Obama ya yi masa wajen kai wa Amurka ziyarar aiki.

A nasa bangaren kuma, shugaba Obama ya furta cewa, yana farin cikin ganin ci gaba da aka samu wajen raya hulda a tsakanin Amurka da Sin a 'yan shekarun baya. Hadin kan bangarorin biyu na da makoma mai kyau, ya kamata su inganta hadin gwiwarsu domin samun ci gaba baki daya.

A ran nan kuma, shugaba Hu Jintao ya gana da takwaransa na kasar Rasha Dmitry Medvedev, inda ya bayyana cewa, kasar Sin na fatan taron koli a karo na hudu na rukuni na G20 zai samu kyawawan sakamako a fannoni daban daban. Ya jaddada cewa, yanzu tattalin arzikin duniya yana samun farfadowa, amma tushensa ba shi da inganci sosai. Kasar Sin tana son kara inganta samun daidaitawa a tsakaninta da kasar Rasha a karkashin tsarin G20 domin bayar da gudummawa ga samun dauwamammen ci gaban tattalin arzikin duniya yadda ya kamata.

A wata sabuwa kuma, a wannan rana, shugaba Hu Jintao ya gana da firaminista David Cameron na kasar Birtaniya, inda shugaba Hu ya jaddada cewa, Sin da Birtaniya suna da moriya daya wajen sa kaimi ga farfadowar tattalin arzikin duniya da tinkarar kalubalen da ke gaban duniya a sakamakon kasancewar illar da matsalar kudi ta duniya da matsaloli daban daban na duniya ke bayarwa. Muddin bangarorin biyu suka kara tattaunawa a tsakaninsu, da lura da abubuwan da suke mai da hankali a kai, kana da warware rikicin da ke tsakaninsu yadda ya kamata bisa tushen nuna girmamawa ga juna da yin zama daidai wa daida, to tabbas ne za a ciyar da huldar abokantaka da ke tsakanin Sin da Birtaniya bisa manyan tsare-tsare gaba.(Kande Gao)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China