in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Bikin baje kolin duniya a Shanghai zai samar da wata kyakkyawar makoma ga Bil'adam
2010-06-26 16:38:38 cri

Ranar 26 ga wata rana ce ta dakin nune-nune na kasar Somaliya a bikin baje kolin duniya a birnin Shanghai. Mataimakin babban wakilin gwamnatin kasar Sin kan bikin baje kolin duniya a Shanghai Jiang Zhengyun da shugaban kwamitin 'yan majalisar man fetur da makamashi na kasar Somaliya Abdullahi Yussuf Ahmed sun halarci bikin daga tutoci a cibiyar dandalin bikin, tare da yin jawabi.

A cikin jawabinsa, Jiang Zhengyun ya waiwayi baya kan dankon zumunci irin na gargajiya dake tsakanin kasashen Sin da Somaliya. Ya yi imani da cewa, dakin nune-nune na Somaliya zai zama wata babbar alama ga bikin baje kolin.

Bayan haka, a cikin jawabinsa, Abdullahi Yussuf Ahmed ya nuna godiya ga kasar Sin da ta kula da tawagar Somaliya yadda ya kamata. Ya ce, a bikin baje kolin, kasar Somaliya za ta nuna al'adunta a duk fannoni, tare da yin musayar fasahohin bunkasa birane da sauran kasashe. Ya yi imani cewa, bikin baje kolin duniya da ake yi a birnin Shanghai a shekarar 2010 zai samar da wata kyakkyawar makoma ga Bil'adam baki daya.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China