in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin za ta fi mai da hankali kan batun ci gaba a taron koli na G20 da za a yi a Toronto
2010-06-23 17:57:38 cri
A ranar 23, Hu Jintao, shugaban kasar Sin ya tashi zuwa kasar Kanada don yin ziyara tare da halartar taron shugabanni a karo na 4 na kungiyar G20, taron da zai gudana a birnin Toronto na kasar. Shugaba Hu ya kai ziyarar ne bisa gayyatar da Michaelle Jean, babbar gwamnar kasar Kanada, da Stephen Harper, firaministan kasar suka yi masa. Sa'an nan za a iya kasa ayyukan da zai yi zuwa kashi 2, wato ziyarar aiki da halartar taron koli na G20. Daga ranar 24 zuwa ranar 26 ga wata, Hu Jintao zai yi ziyara a wurare daban daban na kasar Kanada, inda zai gana da shugabannin kasar, da kuma yin hira da jama'ar kasar na sassa daban daban. A yayin ziyarar shugaba Hu, sassan gwamnatocin 2 da wasu kamfanoni za su sa hannu kan yarjeniyoyi da zummar kulla huldar hadin kai, yarjeniyoyin da za su shafi tattalin arziki, da kiyaye muhalli, da tabbatar da igancin kayayyaki, da al'adu, da dai sauran fannoni daban daban. Kafin fara wannan ziyara kuma, Cui Tiankai, mataimakin ministan waje na kasar Sin, ya bayyana ma'anar ziyarar kamar haka, 'Ziyarar da Shugaba Hu zai yi ta kasance karo na farko da shugaban kasar Sin ya kai a kasar Kanada cikin shekaru 5 da suka wuce, hakan zai zama wani babban dalilin da ya shafi huldar da ke tsakanin kasashen 2, ta la'akari da yadda aka cika shekaru 40 da kulla dangantakar diplomasiyya a tsakanin kasashen 2. Muna tare da imanin cewa, za a cimma nasarori da yawa a wajen ziyarar, bisa kokarin da bangarorin 2 suke yi.'

Za a shirya taron shugabanni a karo na 4 na kungiyar G20 a birnin Toronto na kasar Kanada daga ranar 26 zuwa ranar 27 ga wata, inda za a tattauna kan yanayin da duniyarmu ke ciki wajen gudanar da harkokin tattalin arziki, da matsalar cin bashin da kasashen Turai ke fama da ita, da yadda za a samar da wani tsarin ci gaba mai dorewa, da garambawul din da za a yi wa hukumomin hada-hadar kudi na duniya, hade da sa ido kan cinikayyar da ke gudana a tsakanin kasashen duniya da kuma sassan kudi nasu, da dai makamantansu.

Bisa kokarin da gamayyar kasa da kasa suka yi wajen shawo kan rikicin hada-hadar kudi, sannu a hankali an kafa wani tsari na kungiyar G20 da ya kunshi kasashe masu ci gaban masana'antu, da wasu kasashen da ke saurin tasowa a duniya. A watanni 19 da suka gabata, an shirya tarurukan shugabanni na G20 a biranen Washington, da London, da Pittsburgh. Hakan na da alamun cewa, ana kokarin mayar da taron shugabanni na kungiyar G20 ya zama wani tsari na kullum, sa'an nan ya fara canza matsayinsa daga wani dandalin da ake yin amfani da shi wajen fama da rikici zuwa wata hukumar daidaita tattalin arzikin duniya. Sa'an nan, Cui ya bayyana ra'ayin kasar Sin game da muhimmancin kungiyar G20 cewa, 'Taron shugabanni na kungiyar G20 ya zama wani dandali mai muhimmanci da kasashen duniya ke yin amfani da shi wajen tinkarar rikicin hada-hadar kudi, da kuma karfafa hadin gwiwar da ake yi a tsakanin kasashe daban daban'.

A nasa bangren, Zhang Tao, darektan sashi mai kula da harkokin duniya na baitulmalin kasar Sin , ya furta cewa, 'Ta la'akari da yanayin da ake ciki, taron shugabanni na G20 na da ma'ana sosai a fannin karfafa hadin gwiwar kasashen duniya. Ya kamata kasashe daban daban su dauki manufofin da za su tabbatar da karuwar tattalin arzki a kasashen.'(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China