A ran 20 ga wata, an kammala karawa a zagaye na biyu a rukunin G na gasar cin kofin duniya ta kwallon kafa da ke gudana a kasar Afirka ta Kudu. A cikin gasar ta rukunin G, kungiyar Brazil ta lashe ta Cote d'ivoire da ci uku da daya, bisa nasarar da ta samu har sau biyu, ta sami maki 6, kuma ta fita daga rukuni-rukuni a gasar cin kofin duniya.
A cikin gasanni 2 na rukunin F na gasar wasan kwallon kafa ta cin kofin duniya, kungiyoyin Italy da New Zealand sun yi kunnen doki da ci daya da daya. Kuma kungiyar Paraguay ta lashe ta Slovakia da ci biyu da nema.(Abubakar)