in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kamaru ta zamanto ta farko da za ta bar gasar cin kofin duniya ta Afirka ta Kudu
2010-06-20 18:45:51 cri

Ran 19 ga wata bisa agogon wurin, an kammala karawa a zagaye na biyu a rukunin E na gasar cin kofin duniya ta kwallon kafa da ke gudana a kasar Afirka ta Kudu, wanda ke hade da kasashen Holand da Japan da Denmark da kuma Kamaru.

Kasar Denmark da samu nasara a kan Kamaru da ci biyu da daya. Ko da yake kasar Kamaru ce ta fara samun nasara a wannan wasa a lokacin da shahararren dan wasanta Samuel Eto ya jefa kwallo a ragar Denmark. Amma daga baya kasar Denmark ta rama, sannan kuma ta sake kara wata. Ta haka kasar Kamaru da ta sha kashi har sau 2 ta zamanto ta farko da za ta bar gasar cin kofin duniya a wannan karo.

Har wa yau kuma, kasar Holand ta yi nasara a kan Japan da ci daya mai ban haushi, ta haka bisa nasarar da ta samu har sau biyu, ta zama ta farko da ta fita daga rukuni-rukuni a gasar cin kofin duniya.

Ban da wannan kuma, kasashen Austrliya da Ghana sun yi kunnen doki da ci daya da daya a karawa ta karshe a rukunin D na gasar cin kofin duniya.(Tasallah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China