in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Han Qide ya je ofishin jakadan kasar Nijeriya dake kasar Sin don nuna jejeto ga rasuwar tsohon shugaban kasar Nijeriya Yar'Adua
2010-05-10 21:05:47 cri

A ran 10 ga wata, Han Qide, mataimakin shugaban kwamitin din-din-din na majalisar wakilan jama'ar kasar Sin ya je ofishin jakadan kasar Nijeriya dake kasar Sin, inda a madadin gwamnatin kasar Sin, Han Qihua ya nuna jejeto a game da rasuwar tsohon shugaban kasar Nijeriya Alhajin Umaru Musa Yar'Adua, kuma ya ajiye kambun furanni. A kan littafin nuna jejeto, mista Han Qide ya rubuta cewa, ya nuna alhini ga rasuwar tsohon shugaban kasar. Jakada Bassey U. Eyo, mataimakin shugaban ofishin jakadancin kasar Nijeriya dake kasar Sin ya yi godiya a game da ziyarar. Manyan jami'an ma'aikatar harkokin waje da na ma'aikatar kasuwanci ta kasar Sin su ma sun je ofishin don nuna alhini.(Asabe)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China