A cikin sanarwar, Ban Ki-Moon ya nuna godiya ga goyon bayan da Umaru Yar'Adua ya nuna wa M.D.D a yayin da yake shugaban kasar Nijeriya, kuma Ban Ki-Moon ya nuna godiya ga aikin da Umaru Yar'Adua ya yi a yayin da ya rike shugabancin karba-karba na kungiyar ECOWAS. A sa'i daya kuma, Ban Ki-Moon ya nuna jejeto ga iyalin Umaru Yar'Adua da gwamnatin kasar Nijeriya.
A ran 5 ga wata da dare, a Abuja, babban birnin kasar Nijeriya, Allah ya yi wa shugaban kasar Najeriya Alhaji Umaru Yar'Adua rasuwa. A ran 6 ga wata, Goodluck Jonathan ya yi rantsuwar zama shugaban kasar Nijeriya.(Abubakar)