in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta nuna alhini a game da rasuwar shugaban kasar Nijeriya
2010-05-06 16:04:31 cri

A ran 5 ga wata, Allah ya yi wa shugaban kasar Nijeriya Alhaji Umaru Yar'Adua rasuwa. A ran 6 ga wata, a birnin Beijing, Jiang Yu, kakakin ma'aikatar harkokin waje ta kasar Sin ta bayyana cewa, kasar Sin ta nuna Alhini a game da rasuwar shugaban kasar Nijeriya wadda ya rasu sakamakon dogon rashin lafiya, kuma tana fatan ci gaba da yin kokari tare da kasar Nijeriya don bunkasa dangantakar dake tsakanin kasashen biyu bisa manyan tsare-tsare yadda ya kamata.

Yar'Adua ya kai ziyara ga kasar Sin a shekarar 2006

Madam Jiang Yu ta bayyana haka ne yayin da take amsa tambayoyin manema labaru a gun taron manema labaru da ma'aikatar harkokin waje ta saba yi. Jiang Yu ta furta cewa, muna nuna alhini a game da rasuwar shugaban kasar Nijeriya Alhaji Umaru Yar'Adua, kuma muna nuna jajantawa ga iyalan shugaban da gwamnatin kasar da kuma jama'ar kasar. Alhaji Umaru Yar'Adua ya ba da gudummawa sosai wajen bunkasa kasar Nijeriya da dangantakar dake tsakanin Sin da Nijeriya. Muna fatan yin kokari tare da Nijeriya don ci gaba da bunkasa dangantakar abokantaka dake tsakanin kasashen biyu.(Asabe)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China