in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a ci gaba da samar da jinya kyauta ga mutanen da suka samu raunuka a girgizar kasa da ta auku a gudumar Yushu ta kasar Sin
2010-04-25 16:41:38 cri
Kamfanin dillancin labaru na Xinhua ya ruwaito labarin da ke cewa, an riga an fara daukan matakan sake gina gundumar Yushu inda aka samu aukuwar bala'in girgizar kasa mai tsanani a kwanakin baya. Sa'an nan, Wang Xiaoqin, mataimakin darektan hukumar kiwon lafiya ta lardin Qinghai, ya yi bayanin cewa, za a ci gaba da samar da jinya kyauta ga mutanen da suka samu raunuka a girgizar kasar har su warke sosai.

Wang Xiaoqin ya kara da cewa, an fara samar da jinya kyauta tun ranar 15 ga watan Afrilu har zuwa ranar 15 ga watan Mayu mai zuwa. Sai dai game da wadanda ba su warke sosai ba bayan wata daya, za a ci gaba da kula da su har su warke sarai, kuma ba tare da karba musu kudi ba.

Alkaluman da aka rawaito mana sun shaida cewa, zuwa ranar 24 ga watan Afrilu, girgizar kasa da ta auku a gundumar Yushu  ta yi sanadiyyar mutuwar mutane 2203, da bacewar wasu 73, sa'an nan an samu mutane fiye da dubu 10 da suka samu raunuka a wajen bala'in. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China