in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
(Sabunta) Kasa da kasa na ci gaba da nuna jaje game da bala'in girgizar kasa da ya abku a gundumar Yushu ta lardin Qinghai a kasar Sin
2010-04-23 20:52:28 cri
A ranar 22 da ta 23 ga wata, an kara samun shugabannin wasu kasashe ko na kungiyoyin shiyyoyi da dama da suka aike da sakwanni ga shugabannin kasar Sin, domin nuna jaje ga gwamnatin Sin da jama'arta game da bala'in girgizar kasa da ya abku a gundumar Yushu ta lardin Qinghai a kasar Sin.

Shugaban kasar Kenya Mwai Kibaki ya nuna tausayawa da jajantawa jama'ar kasar Sin, kuma ya bayyana cewa, jama'ar kasar Kenya da ta kasar Sin za su hada kai tare.

Haka kuma shugabanni na kasashen Namibiya, Togo, Tunisiya, Afrika ta tsakiya, Morocco, Burundi da Djibouti sun nuna jaje ga jama'ar kasar Sin, kuma sun nuna imanin cewa, gwamnatin Sin da jama'arta za su iya cimma nasara wajen saukaka radadin bala'i daga indallahi.

Kana ofishin sakatariya na kungiyar raya kudancin kasashen Afrika wato SADC ya nuna jaje ga gwamnatin Sin da jama'arta da dangogin wadanda suka mutu.

Dadin dadawa kuma, kwanan baya, kasashen Belgium da Romaniya su ma sun mika jaje ga kasar Sin.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China