Ofisoshin jakadancin kasar Sin dake kasashen waje sun nuna alhini ga mutuwar mutane a sakamakon girgirzar kasa da ta abku a yankin Yushu
A ran 21 ga wata, an gudanar da zaman makokin mutanen da suka mutu a sakamakon girgizar kasa da ta abku a yankin Yushu na lardin Qinghai. Kazalika dukkan ofisoshin jakadancin kasar Sin dake kasashen waje sun saukar da tutocinsu zuwa rabin sanda da gudanar da lamura iri daban daban don nuna alhini ga rashin mutanen da aka yi sakamakon girgizar kasar.(Zainab)