Yawan mutane da suka mutu a sakamakon girgizar kasa da ta abku a yankin Yushu ya kai 2187
Bisa labarin da kamfanin dillancin labaru na Xinhua ya bayar, an ce, ya zuwa ranar 22 ga wata da karfe 5 na yamma, girgizar kasa da ta abku a yankin Yushu na lardin Qinghai na kasar Sin ta haddasa mutuwar mutane 2187, da bacewar mutane 80, kuma mutane 12135 sun ji rauni, 1434 daga cikinsu sun ji rauni mai tsanani.
A ran 14 ga wata, girgizar kasa mai karfin maki 7.1 bisa ma'aunin Richter ta abku a yankin Yushu dake lardin Qinghai na kasar Sin.(Zainab)