in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wata jami'ar MDD ta nuna yabo ga gwamnatin kasar Sin da ta yi namijin kokarin ba da ceto
2010-04-22 10:27:15 cri

A ran 21 ga wata, babbar direktar hukumar kula da harkokin ba da ilmi da kimiyya da fasaha da al'adu ta MDD wato UNESCO Irina Bokova ta bayyana cewa, gwamnatin kasar Sin ta yi namijin kokari wajen gudanar da aikin ceto a yankin Yushu na lardin Qinghai.

Madam Bokova ta bayyana wa 'yan jarida a wannan rana cewa, ta nuna alhini ga mutuwa da raunatar mutane masu yawa a sakamakon girgizar kasa da ta abku a yankin Yushu. Ta ce, bayan abkuwar girgizar kasar, tana sa lura sosai kan halin da ake ciki a yanki mai fama da bala'in. Ta gano da cewa, yanki mai fama da bala'in ya dala iyakar teku sosai kuma ana sanyi sosai a yankin, sabo da haka, ana fuskantar matsaloli masu yawa yayin da ake gudanar da aikin ceto. Amma gwamnatin kasar Sin ta yi kokarin ceton mutane masu fama da bala'in.

A ran 21 ga wata, an gudanar da aikin nuna alhini ga mutane da suka rasu a sakamakon girgizar kasa a dukkan kasar Sin. A wannan rana, Bokova ta sake nuna ta'aziyya ga mutane da suka mutu a yankin Yushu.

Madam Bokova ta taba mika wata wasika ga firaministan kasar Sin Wen Jiabao, inda ta ce, idan kasar Sin tana bukatar wani abu daga hukumar UNESCO, to za ta ba da gudummawa ga yanki mai fama da bala'in.(Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China