in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
(Sabunta) Kasashen duniya sun ci gaba da nuna jaje game da bala'in girgizar kasa da ya abku a gundumar Yushu ta lardin Qinghai a kasar Sin
2010-04-21 20:59:31 cri

A ranar 20 da ta 21 ga wata, an kara samun shugabanni na kasashen duniya ko na kungiyoyin shiyyoyi da dama da suka aika da sakwanni ga manyan shugabannin kasar Sin, domin nuna jaje ga gwamnatin Sin da jama'arta game da bala'in girgizar kasa da ya abku a gundumar Yushu ta lardin Qinghai a kasar Sin.

Shugabanni na kasashen Benin, Tanzania, kamaru, Burundi, Somaliya sun jajantawa jama'ar kasar Sin da dangogin wadanda suka mutu, kana sun yaba wa matakan da gwamnatin Sin ta dauka domin saukaka radadin bala'in girgizar kasa da ceton mutane.

Babban jami'in da ke kula da harkokin 'yan gudun hijira na M.D.D Antonio Guterres da sakatare janar na kawancen kasashen Larabawa Amar Mahmoud Moussa sun nuna jaje ga dangogin wadanda suka mutu, kuma sun yi fatan wadanda suka jikkata za su samu waraka cikin hanzari, kazalika sun nuna imani cewa, gwamnatin Sin da jama'arta za su iya wajen warware matsalar da bala'in girgizar kasa ya haifar.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China